الخميس، رمضان ٢٣، ١٤٣١

Allah Ya raya Balan Bara'atu.FW: Muhimman Labarai Daga Muryar Amurka

Manyan Labarai

Yaki Ya Kare A Kasar Iraqi

Shugaba Barack Obama na Amurka ya bayyana cewa daga wannan rana, Amurka ta kawo karshen dukkan matakan soja a kasar Iraqi

Shugaba Barack Obama yana jawabi ga Amurkawa Talata, 31 Agusta, 2010

Mahaukaciyar Guguwa Mai Ruwan Sama Ta Earl Ta Ratsa Ta Tsibiran Puerto Rico da British Virgin Islands

Jami'ai sun ce wannan mahaukaciyar guguwa tana tafe da iska mai juyawar kilomita 215 cikin awa daya

Hoton mahaukaciyar guguwa ta Earl tun lokacin da ta fara kankama a kan teku daga tauraron dan Adam

Mataimakin Shugaban Amurka Joe Biden Yana Iraqi

A yau talata Amurka zata kawo karshen dukkan ayyukan farmaki a kasar Iraqi, daya daga cikin alkawuran da shugaba Barack Obama yayi.

Shugaba Barack Obama Na Amurka Yace Bai damu Da Masu Cewa Shi Musulmi Ba Ne

A cikin hira da gidan telebijin na NBC, shugaban na Amurka ya yi magana kan tattalin arziki da kuma jita-jitar da wasu ke yadawa a kansa

Shugaba Barack Obama na Amurka

Ambaliyar Ruwa Ta Raba Mutane Dubu 200 Da Matsugunansu A Jamhuriyar Nijar

Majalisar Dinkin Duniya ta yi rokon da a tallafawa Nijar da gaggawa saboda ambaliyar da ta biyo bayan mummunan karancin abinci a kasar

Wata yarinya mai suna Fadima Daniri tana jiran ruwa domin shayar da dabbobinta a Gadabeji a Jamhuriyar Nijar. A bayan wannan karancin ruwa da kasar ke fuskanta kuma, sai ga ambaliyar ruwa ta kara jefa dubbai cikin halin kaka-ni-ka-yi.

Masu Tsattsauran Ra'ayin Addini Sun Hallaka Yan sanda

Wasu da ake Tsammanin Masu Tsattsauran Ra'ayin Addinin Musulunci ne sun Hallaka 'Yan Sandan Nijeriya.

Wasu Yan sandan Nijeriya kenan a bakin aiki. (File Photo)

Yak'i da fataken mata a Najeriya da Cote d'Ivoire

Kungiyar kare hakkokin bil Adama ta Human Rights Watch ta ce a tashi haik'an a yak'i 'yan k'asashen Cote d'Ivoire da Najeriya masu...

A billboard encouraging young women to fight against prostitution and human trafficking in Benin City, Nigeria.

Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya Yace Tilas Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Su San Yadda Za Su Hana Fyade A Kwango

A saboda munin fyaden da 'yan tawaye suka yi wa mata fiye da 150 a wani kauyen Kwango ta Kinshasa Kwamitin yace tilas a yi wani abu.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban-Ki-moon, yace irin wannan fyade da aka yi a kasar Kwango ta Kinshasa ba abu ne da zai karbu ba, kuma tilas a hukumta wadanda suka aikata shi.

An Umurci Dubban Mutane su Tashi

Jami'an gwamnatin Pakistan sun Umurci Dubban Mutane su Gudu, a Sa'ilinda Ambaliyar Ruwa ke Dada Munana.

Mutanen da ambaliyar ruwa tab tsugunnar a Pakistan

Iyalan Shugaban Tsagerun Naija-Delta Sun Tabbatar Cewa An Kashe Shi

IYalan shugaban mayakan sa kan Naija-Delta sun ce an masa kofar rago ne aka kashe shi.

Yan tawayen yankin Niger Delta na Nigeria mai arzikin man fetur. (File Photo)
Karin Labarai

A cikin Wannan Email Din:

Labarai
Najeriya
Afirka
Sauran Duniya
Kiwon Lafiya

Cire Sunanka/ki

Idan an gaji da samun Kanun Labaranmu ta Email, to ana iya cire suna ko adireshi a nan Cire Sunanka/ki

Ana Bukatar Taimako?

Idan ana da wata tambaya game da Kanun Labaran nan, ana iya aika sako ga: Sashenhausa@VOANews.com

Mun sake tsarin dandalinmu domin ku samu saukin gano labarai, rahotanni, shirye-shirye, ko kuma sauti da bidiyo da hotunan da kuke bukata. Kuna iya aiko mana da ra'ayoyinku kan wannan sabon tsari namu zuwa ga: sashen-hausa@voanews.com

Cire Sunanka/ki


ليست هناك تعليقات: