الثلاثاء، ربيع الأول ٠٤، ١٤٤٥

MALAM SHEHU YUNUSA ALLAH YA MASA RAHAMA.

Abdu Bello na Hamza: Allah Ya ji qan Mal. Shehu Yunusa da mu ka yi sallar janazar sa da safiyar yau Talata 19 September 2023. Allah ya sa ya huta, ya ji qan iyayen mu da magabatan mu. Allah ka yi mana kyakkyawan qarshe da kyakkyawar makoma. Alhamdu lIllah.

الجمعة، صفر ٢٣، ١٤٤٥

Bilqeesu Abdulkarim Rishi

Assalamu alaikum, Masoya, yau Juma'a 08 sept 2023 ne sunan 'ya ta kuma na sa mata Bilkees. a sa ta a addu'a. ku ma Allah ya cika muku burin ku. ABDU BELLO RISHI. https://www.facebook.coum/jibwisbauchi/videos/883780626493867/?mibextid=JgRRn7n7jRVACbyL

الأحد، صفر ١٨، ١٤٤٥

MAI SHAFI

Assalamualaikum Alhaji jiya na dawo daga juma'a 1-sept-2023 na samu an haifa min yarinya, ina sa rai zan sa mata ko na sanya mata suna Bilqeesu, da fatan Alhaji kar a manta ta da mu a cikin addu'a. http://islamport.com/l/srh/2210/165.htm ABDU BELLO RISHI

An haife ni ne a unguwar kirgi a garin Rishi, a wajejen 1970, Nayi Primary a Rishi Primary School 1976-1983 don nayi repeating a aji biyu, nayi form one a Government Day Junior SECONDARYSCHOOL Gumau, form two da three kuma a Day Junior Secondary School Tulu inda na kammala junior three na a 1986, da ma a duk halin School din da na ke zuwa bai hana na dawo weekend ko hutu na ci gaba da zama wa mahaifina Muhammad Bello a gun treda ba, sai dai bai yarda na fara zuwa gona ba sai a 1986, kuma duk da cewa in ba lalura ko hidima ba, bai fiya fashin zuwa kuza ba har ya bar duniya Allah ya masa Rahma amma bai yarda ni na yi kuzar ba.
A lokacin da na ke makaranta a Tulu ne, Goshin zan gama a 1986, wata rana an taso daga kwallon kafa (Football) sai na biyo wani Bala Dan Borno wani yaron Jos, yanzu ban san in da ya ke ba,
To da na bi sai naji karatun sallarsa dalla dalla a sallar magrib, ya ban shaawa, kasancewar na iya karanta da rubuta wasika da bakaken larabawa sai naji karatun na sa ya fito da ko wane baki, da ma Mallam Danladi hayin kamfani(Baban Awwalu mai kemes "da na ke addu'ar Allah Ya ban 'yar sa khadija, ta farko a mata, ta 4 a haihuwa") Allah yai ma shi Malam Danladi Rahma, shi ya koya mana hatta wasika tun bamu zo Aji 5 (class five) ba, burge nin da karatun yayi ne ya sa ina dawo gida weekend, sai na cewa Abdul’aziz (Abokina ne) muje mu sayo kawa’idi mu je makaranta shi ko bai yi musu ba, muka sayi kawa’idi mu ka je makarantar Mallam Abdu Liman (Allah ya kara masa son Annabi) yayan Alhaji Shayabo, kuma shine babban limamin Rishi, shine uban Batulu, Nafisah, Hadi, nazir, Shema-u, Amina da Bakari, dukkan su Hafsatu ta haife su, Babban ‘Dansa kuma Awwalu Rabin Ummaru Na anka ce ta haife shi.

To Ni da Abdul-Aziz muka kama zuwa makarantar Mallam Abdu Liman, har mun sauke kawa-idi da Alhari, littafin da ake farawa da su a makarantun zaure na asali a nan Nigeria ta Arewa, saukewar mu Ahlari ke da wuya sai samarin gidan su Abdul-Aziz su ka shiga Izala (lokacin ba ta rabu biyu ba) har da shi.
Shigar sa Izala ke da wuya, sai ya dinga jin kunyar zuwa Makarantar Mallam Abdu liman don ’Dan ‘Darika ne ta tijjaniyya.
A 1987 na fara fita yawon duniya, Inda na kwana biyu a Jos, Arba-in da shida a tsakanin Ladin Makole da kode, ranar 1st October 1987 na isa Birningwari, daga Kaduna zuwa B/gwari Naira 10 a Peaguet.
Nayi Tallen rake da Gwaiba a B/gwari, musamman ma Gwaiba, don garin Akwai gwaiba kewaye da shi.
2 – Jan – 1988 Ranar Taron dukkan Musulmin Nigeria a kaduna da na samu halarta, na dawo gida na iso Rishi Ranar lahadi da safe sai ga yayata sa’a daga maraku da rana, da yamma sai ga yaya na Garba daga ladinmakole duk kan su sunzo Bikin Auren kanwata Bebi wanda akai a watan na January, lallai ranar farin chiki ya lullube Mahaifina Bello ganin ga ni dansa da ya Haifa na dawo daga fitan da na kwana 139 ba na gida, Ga kuma sa’a da Garba ‘ya’yan yayan sa Abdullahi da ya sha mama ya bar mar (ya rasu tun ba a haifeni ba) Alhamdu Lillahi, yawon da na yi ya sa ido na ya bude fiye da da, inda dawo wa take da wuya a 1988 na karanta da sauke kawa-idi, Ahlari, Ashmawi, Daka-ikul’Akhbar, zabura, Izziyya, Risala, Ihya-ussunnah da nurul-albab.
Wannan ‘Dan karatun, da kuma tajwiydin surorin Nasr da kafirun da kausar a gun Mallam Suleidaini a Rishin kuma ga ni da nacin saurare da bin filin koyon karatun Alkur-ani mai Girma a Tashar R.N.K da shirin Turaki Aliyu Misau' Rayuwar Musulmi' da dai ‘dan Abin da ba za a raina ba, na gina 'yar fahimtar karatun Addini na da nake dan yi A yau,

Aure na
Na auri Maimunatu ‘yar Marigayi Abdun Jana, kuma goyon Alhaji Sabo Maimaganin turawa a Ranar 6-12-1993, mun rabu a watan October – 1998.
Na auri Wasilan Wada (Ririwai) shekarar mu guda Na rabu da ita, bayan tayi wata shida a Rishi wata shida a Jos.
Ranar 4-ga watan Zulhijjah 1425 na auri Zainab yar Shehu Tawul kuma 1 zuwa yau 3-j-sani 1427 muna tare ko da yake tarewarta a guna Ranar 4/June/2005 ne anan Jos, muna fatan Allah ya bamu rabo Amin.

HAIHUWAR DA NA YIMaimuna ta Haifa min Musa ranar Alhamis din wata Oktober 1995, yanzu haka ya na gun mahaifiya ta Talle (Habiba) a primary 4 a nan Gangare Jos.
har wa yau ALLAH YA ARZUTA NI DA MUHAMMAD BELLO DA ZAINABUN DA MUKE TARE TA HIFA MIN RANAR 13/03/2007

DANGIIna da kanwa 34 da muke uba daya, ta na zawarci a Unguwar Rogo ‘ya’yan ta 4 ina da kanwa Balkis 31 ta na aure a Rikkos uwarmu ’daya ,da kani Muhammad kabir 28 yana karantar da yara a onacan inyamurai, Hafsatu 23 tana aure a kusa da Dambam da yara 3, Binta 20 uwar mu daya tana aure anan tGangare yaron ta daya Haruna, Nafi 18 uwar mu ’daya tana aure a nan Gangaren Jos ’danta ’daya Suleiman.

SANA’ A TA
A yanzu haka (July 2006:- J/SANI 1427) ni Dandako ne a yankolli umuwman a shagon Alhaji Sule Nayaya khusuwsan, muna sauke suga, fulawa, shinkafa, dukkan su dai suna zuwa muna sauke wa da ku

[7/23, 1:33 PM] +234 706 680 3205: TSAKANIN KIMIYYA DA SUNNAH AKAN KISAN TSAKA
Wani ɗan uwa ya yi min tambaya akan tsaka cewa wai a ina
aka ce tana da guba a cikin hadisi? Sai na ce masa ban sani
ba. Daga baya sai na ga ashe ana ta zance ne akan tsaka
sakamakon wani labari da BBC Hausa suka buga. Duk da ba na
son shiga irin wannan sabgogin amma dai ina da wani ta'aliƙi
kamar haka.
A cikin hadisai mabanbanta Manzon Allah (SAW) ya yi umarnin
cewa a kashe tsaka tare da ambaton ta a matsayin sheɗaniyar
halitta.
Daga cikin hadisan akwai hadisin Bukhari da Muslim wanda
suka ruwaito daga Ummu Sharik da take cewa: "Manzon Allah
(SAW) ya yi umarni da a kashe tsaka sannan ya ce: ita tsaka ta
kasance ita ce kaɗai dabbar da ta dinga ƙoƙarin hura wutar da
kafirai suka yi nufin ƙona Annabi Ibrahim (AS) a cikinta".
Abubakar Ibnul Arabiy yana cewa: "Wannan yana nufi izuwa ga
cewa cutarwa wata ɗabi'a ce ta dindindin a wajen tsaka"
A wata riwaya ta Ahmad da Ibnu Majah da Ibnu Hibbana
(wannan lafazinsa ne) cewa aka yi wata bararriyar baiwar Al-
Fakih Ibnul Mugee
[7/23, 1:38 PM] alfanu: https://chat.whatsapp.com/CfYgrzNexhWKaXfrQOL3j9